Days of Remembrance

Hausa · Bahá'u'lláh

Ziyāra BH02307

Add range:

Wannan āyā, ana jan ta a ƙabarin Baha’u’llah, kō na Bab (tsīra da aminci su tabbata a garēsu). Wanda yake sō, yana iya karantā ta, rānēkun haifuwarsu.

Yabo dake dangance da zamantakēwarka mai martaba, kuma da mahibbar da ta haskō daga ƙyalƙyalin kyāwonka, su tabbata a garēka, yā kai da kai nē alāmar girma, da kai nē sarkin dawwama har abada, kuma da kai nē Ubangijin duk abūbūwan dake ƙasa da sammai !

Nā shaida cēwa, ta garēka nē, mulkin Ubangiji Allah, martabarsa da girmansa, suka bayyana, taurārun sāfiyar kyaukyāwar dauri, suka baza haskensu da bā ya shūɗēwa, cikin samāniyar kudurinka, kuma kyāwon wanda bā ya ganuwa, ya haske jiririn halitta.

Nā shaida kuma da cēwa, daga rubūtun alƙalaminka guda, sai umarninka « kasance » ya aikata, ɓōyeyyen gaibun Ubangiji Allah ya bayyana, ka rāya duka halittu, kuma duka wahāyi ya sauko.

Nā shaida cēwa, ta kyāwonka nē, kyāwon wanda shīnē abun yabo ya bayyana, kuma ta fuskarka cē, fuskar wanda shīnē abun ƙauna ta fitō hīli, kuma da kalmā guda, ka ƙayyada matsayin duk halitta, ka ɗaukaka wanɗanda suka yi īmāni har zuwa ƙōli, kuma ka jēfa kāfirai cikin rāmi mai zurfi.

Nā shaida cēwa, wanda ya amince da kai, yā amince da Allah Ubangiji Subahānahu wa ta āla, kuma wanda ya kai garēka, yā kai ga Ubangiji Allah. Albarka ta tabbata ga wanda ya yarda da kai kuma da alāmunka, ya gwada tawāli gaban martabarka, kuma ya sāmu sāduwa da kai, ya cinma bukātunka, ya jāƙuɗo kusanka, kuma ya durƙusa gaban karagarka.

Hallaka ta tabatta : ga wanda ya ɗauki zunubi garēka, ya yi wātsi da kai, ya yi jīfa da alāmunka, ya ƙi yarda da martabarka, kuma ya tāshi ya kai maka hari, ya gwada girman kai a gabanka, ya ƙi karɓar shaidōdinka, ya kēɓēwa dōkōkinka, ya yi adāwa da ikonka, ya shiga cikin kāfiran nan da sūnāyansu suke rubūce bisa tsarkakkun allunan ƙudurarka.

Daga dāmar rahamarka da alhērinka, ka sauko mani, yā Allah Ubangijina, abun ƙaunāta, tsarkakakkar bazarar alhērinka, dōmin ta ƙēɓē ni da nī kaina, kuma da dūniya, sabōda ta jāgōrancē ni wajen dandalin kusantarka da kaiwa garēka. Kana da īkon aikata abun da ka ga dāma, hakīka, kai nē bisa ga kōmi da kōwa.

Ambatar Ubangiji Allah, da yabonsa, ɗaukakarsa da girmansa su tabatta a garēka, yā kai wanda kai nē kyāwonsa ! Nā shaida da cēwa, bābu idon halittar da ya kalli wanda aka zālunta kamar kai. Duk rāyuwarka, an zunduma ka cikin tēkun rūdāni. A wani lōkaci, an ɗaure ka da sarƙa da mari, a wani lōkaci kuma, maƙiyyanka sun zāre maka takubbansu. Amma, duk da haka, kā gayyaci mutāne, da su bi umarnin da wanda shīnē al’alīmu, mai hikima maras iyāka, ya sauko a garēka.

Ina rokon Ubangiji, da ya karɓi rūhūna, tamkar tōshi, dōmin wahalōlin da ka gabāta, kuma ya amshi raina sabōda adāwar da aka maka. Ina roƙon ka, don darajarka da waɗanda fuskarsu ta sāmu ƙyalƙyalin hasken fuskarka, waɗanda don matuƙar ƙaunarka, suka karɓi duk abūbūwan da ka umarcē su da yi, ka kēta lābilen da ya raba ka da halittarka, kuma ka bā ni alhērin dūniya da na lāhira. A gaskiya, kai nē al’azīzu, kai nē al’alīyu, mafi ɗaukaka, mai gāfartāwa har kullun, mai jin-ƙai.

Yā Ubangiji Allāna, ka albarkatar da itāciyar Ubangiji, da ganyenta, da rassunta, da tsironta, da karanta, da ƴāƴanta, har iyākar tsawon sūnāyenka māsu martaba, da laƙanunka mafi ɗaukaka. Ka kāre su, da harin maƙiya, da rundunōnin azzālumai. A gaskiya, kai nē al’azīzu, al ƙādiru. Yā Allāna, ka albarkatar da bāyinka maza da māta, da suka isō garēka. A gaskiya, kai nē mai rahama, wanda alfarmarsa bā ta da iyāka.

Bābu wani Allah illa kai, mai gāfartāwa a kullun, mayalwaci.

Tsāme Daga Bukin Rānekun Tuāwa BH05154

Add range:

Rānar haifuwar Baha’u’llah (aminci ya tabbata a garēshi)

Shīnē tsarkakakke, maɗaukaki, Mafi girma

Rānar bukin karramāwa cē, wandan shīnē kyāwon Ubangiji Allah, jabbāru, mai īko, mai ƙauna, yā hau gadon īkonsa. Murnā ta tabbata ga wanda, a wannan rānā ya kai garēshi, kuma wanda Allah, mai cēto cikin matsala, madawwami, ya dūbi wajensa. Ka cē: Mun karrama wannan buki cikin kurkuku mafi girma, a lōkacin da sarākunan dūniya suka tāshi suka yāƙē mu. Ammā fa, ƙarfin azzālumai har abada bā ya iya jā da mu, kuma rundunōnin dūniya har abada bā su iya murƙushe mu. Haka Arrahamānu yake shaidāwa.

Ka cē: ashē yā cancanta a tūre tūshen hakīkantaka gaban sūrūtan al’ummōmin dūniya? Ā’ā, nā rantse da kyāwonsa dake haske duk abūbuwan dā da na gōbe! A gaskiya wannan cē alfarmar Ubangiji da take lulluɓē duk halitta, kuma haka nē īkonsa da ya mallaki duk abūbuwan dake gani da duk abūbuwan da ake gani. Ku riƙe igiyar muhimmin īkonsa, kuma ku ambaci Ubangijinku mai ƴanci, a wannan assubāhi da haske yake gwada duk gaibu ɓōyeyye. Haka nē madawwami ya faɗa a wannan rānā da aka būɗe zāɓeɓɓen ruwa. Ku yi hattara, kada tunānin shirmen waɗanda suka ƙi yarda da Allah su tāda hankulanku, kō kuma zatuttukansu na wōfi, su nīsantā ku da madaidaiciyar hanya.

Yā kē al’ummar Baha! bisa fukāfukan dangana, ki hira ki shiga cikin sararin ƙaunar Ubangijinki, mai rahama, kuma ki tāshi dōmin ki kai Ubangijinki ga nasara, kamar yanda ādanannun alluna suka ƙadarta. Kada ki yi jāyayya da kōwa cikin bāyūna. Ki mīƙā musu zāƙin tsarkakakkun kalmar Ubangiji, sabōda, da īkonta nē mutāne suke iya sāmun dāmar jūyāwa wajensa. Duk waɗanda a yau, ba su kula da Allah ba, sun ɓata cikin shāwarsu, cikin ba su mā gāne ba. Murna ta tabbata ga wanda, cikin ƙasƙanta da tawāli’u, ya jūya fuskarsa wajen assubāhin āyōyin Ubangijinsa.

Yā cancanta ka tāshi ka karantar da mutāne bisa abun da aka bayyana cikin kitābin Ubangijinsu, mai īkō, mai ƴanci.

Ka cē: ka ji tsōron Allah, kuma kada ka kula da zatūttukan wōfi da waɗanda suke tafiya bisa hanyar shakka da rishin ādalci suke faɗa. Da zuciya mai armashi, ka jūya wajen fādar Ubangijinka, mamallakin duka sūnāye. A gaskiya, zai taimakē ka da ƙarfin gaskiya. Bābu wani Allah illā Shī, mai īko, mai cikakkiyar kyauta.

Yana yiyuwa ka gaugauta zuwa ga ƙaramin tabki, alhāli gā babban tēku nan gaban idonka? Ka jūyā gabādayanka wajensa, kada ka bi sāwun kōwanne daga cikin kāfirai maƙaryata. Tsuntu madawwami nā wāƙā bisa rassun itāciyarmu ta Ubangiji. Nā rantse da Ubangiji Allah! wāƙarta guda ɗaya tak, tā isa ta shāwar da majalasar samāniya, har mā, mazaunan birānen sūnāye, kuma har mā waɗanda suke zāgayāwa, suna kēwaya gadon mulki sāfe da marēce.

Haka nē, ruwan kalmōmi yake zubōwa daga samāniyar ƙudirin Ubangijinka, mai rahama. Ku jākuɗo kusanta, yā ku al’umma, ku yi wātsi da waɗanda suke gardama ta wōfi da banza bisa āyōyin da Allah ya sauko, kuma da suka ƙi yarda da Ubangijinsu da ya zō musu ɗauke da hujja da shaida.

(Ayyam-i-Tis’ih shāfi 45-47)